Ezra 2:1-70

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

1Ga lissafin waɗanda suka dawo daga bauta a Babilon, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwasa zuwa bauta a ƙasar Babilon (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowa ya koma garinsu.

2Sun komo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Serahiya, da Re’elaya, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba’ana). Ga jerin mazan mutanen Isra’ila.

3Zuriyar Farosh mutum 2,172

4ta Shefatiya 372

5ta Ara 775

6ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,812

7ta Elam 1,254

8ta Zattu 945

9ta Zakkai 760

10ta Bani 642

11ta Bebai 623

12ta Azgad 1,222

13ta Adonikam 666

14ta Bigwai 2,056

15ta Adin 454

16ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98

17ta Bezai 323

18ta Yora 112

19ta Hashum 223

20ta Gibbar 95.

21Mutanen Betlehem 123

22na Netofa 56

23na Anatot 128

24na Azmawet 42

25na Kiriyat Yeyarim, da Kefira Beyerot 743

26na Rama da Geba 621

27na Mikmash 122

28na Betel da Ai 223

29na Nebo 52

30na Magbish 156

31na ɗayan Elam ɗin 1,254

32na Harim 320

33na Lod, da Hadid da Ono 725

34na Yeriko 345

35na Sena’a 3,630.

36Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973

37ta Immer 1,052

38ta Fashhur 1,247

39ta Harim 1,017.

40Lawiyawa. Lawiyawa na zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodawiya) mutum 74.

41Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 128.

42Masu tsaron haikali. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita, da Shobai mutum 139.

43Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,

44Keros, Siyaha, Fadon,

45Lebana, Hagaba, Akkub,

46Hagab, Shamlai, Hanan,

47Giddel, Gahar, Reyahiya,

48Rezin, Nekoda, Gazzam,

49Uzza, Faseya, Besai,

50Asna, Meyunawa, Nefussiyawa,

51Bakbuk, Hakufa, Harhur,

52Bazlut, Mehida, Harsha,

53Barkos, Sisera, Tema,

54Neziya da Hatifa.

55Zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, Hassoferet, Feruda,

56Ya’ala, Darkon, Giddel,

57Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Ami.

58Dukan zuriyar ma’aikatan haikali, da kuma bayin Solomon 392.

59Waɗannan mutanen ne suka zo daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addan da Immer, amma ba su iya nuna ainihin tushensu daga Isra’ila ba.

60’Yan zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 652.

61Daga cikin firistoci kuma, zuriyar Hobahiya, Hakkoz da Barzillai (wanda ya auri diyar Barzillai mutumin Gileyad da ake kuma kira da wannan suna).

62Waɗannan sun nemi sunayen iyalansu a cikin littafin da ake rubuta sunayen amma ba su ga sunayensu ba, saboda haka sai aka hana su zama firistoci domin an ɗauka su marasa tsabta ne.

63Gwamna ya umarce su cewa kada su ci wani abinci mai tsarki sai firist ya yi shawara ta wurin Urim da Tummim tukuna.

64Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,

65ban da bayinsu maza da mata 7,337; suna kuma da mawaƙa maza da mata 200.

66Suna da dawakai guda 736, alfadarai 245,

67raƙuma 435, da jakuna 6,720.

68Sa’ad da suka isa haikalin Ubangiji a Urushalima, sai waɗansu shugabannin iyalai suka yi bayarwar yardar rai ta gudummawarsu domin sāke gina gidan Allah a wurin da yake.

69Bisa ga ƙarfinsu suka bayar da darik 61,000 na zinariya, da maina 5,000 na azurfa, da rigunan firistoci guda 100.

70Firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali, tare da waɗansu mutane, da dukan sauran Isra’ilawa suka zauna a garuruwansu.