Ayuba 25:1-6
Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
1Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”