Zabura 102:1-28

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

1Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.

2Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.

3Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.

4Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.

5Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.

6Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.

7Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.

8Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.

9Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye

10saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.

11Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.

12Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.

13Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.

14Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.

15Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.

16Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.

17Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.

18Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,

19“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,

20don yă ji nishe-nishen ’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”

21Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima

22sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.

23Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.

24Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.

25A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.

26Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.

27Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.

28’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”