Zabura 113:1-9

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

1Yabi Ubangiji. Ku yabe shi, ya ku bayin Ubangiji, ku yabi sunan Ubangiji.

2Bari a yabi sunan Ubangiji, yanzu da har abada kuma.

3Daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa, a yabi sunan Ubangiji.

4Ana ɗaukaka Ubangiji a bisa dukan al’ummai, ɗaukakarsa a bisa sammai

5Wane ne yake kamar Ubangiji Allahnmu, Wannan mai zama a kursiyi can bisa,

6wanda yake sunkuya yă dubi sammai da duniya?

7Yakan tā da matalauta daga ƙura yakan ɗaga mabukata daga tarin toka;

8ya zaunar da su tare da sarakuna, tare da sarakunan mutanensu.

9Yakan zaunar da matar da ba haihuwa a gidanta ta zama kamar mahaifiyar ’ya’ya mai farin ciki. Yabi Ubangiji.