Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
1Yabi Ubangiji, dukanku bayin Ubangiji waɗanda kuke hidima da dare a gidan Ubangiji.
2Ku tā da hannuwanku a cikin wurinsa mai tsarki ku kuma yabi Ubangiji.
3Bari Ubangiji, Mahaliccin sama da ƙasa, ya albarkace ku daga Sihiyona.