Zabura 3:1-8
Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
1Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” Sela
3Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. Sela
5Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. Sela