Zabura 61:1-8

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

1Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.

2Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.

3Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.

4Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. Sela

5Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.

6Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.

7Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.

8Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.