Zabura 11:1-7
Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
Allah Madaukaki yana kare masu adalci
Copyright (c) 2009, 2020 Biblica, Inc. CC BY-SA 4.0.
1A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon ’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.