Zabura 129:1-8
Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
Ubangiji ya 'yantar da mai magana daga mugaye
Copyright (c) 2009, 2020 Biblica, Inc. CC BY-SA 4.0.
1Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
2sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
3Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
4Amma Ubangiji mai adalci ne; ya ’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
5Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
6Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
7da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
8Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”