Zabura 129:1-8

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

Ubangiji ya 'yantar da mai magana daga mugaye

Copyright (c) 2009, 2020 Biblica, Inc. CC BY-SA 4.0.

1Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,

2sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.

3Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.

4Amma Ubangiji mai adalci ne; ya ’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.

5Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.

6Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;

7da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.

8Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”