Zabura 67:1-7

Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)

1Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, Sela

2don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.

3Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.

4Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. Sela

5Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.

6Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.

7Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.