Zabura 81:1-16
Biblica Open Hausa Contemporary Bible (BSRK)
1Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an ’yantar da hannuwansu daga kwando.
7Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. Sela
8“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”